Gawar tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Nasarawa kuma tsohon ƙaramin Ministan Birnin Tarayya (FCT), Sanata Solomon Aku Ewuga, ta iso Najeriya daga kasar Masar inda ya rasu yana da shekaru 70.
Ewuga, wanda ya wakilci jihar Nasarawa ta Arewa a Majalisar Dattawa ta 7, ya rasu ne a ranar Talata, 23 ga Satumba, 2025.
Gawar Ewuga ta iso Najeriya ne a ranar Alhamis ta filin jirgin saman kasa da kasa na Nnamdi Azikiwe, Abuja.
- Kungiyar Mata Lauyoyi Ta Yi Zanga-zangar Kin Amincewa Da Bukatar Sauya Kwamishinan Yan Sandan Kano Da Gwamna Abba Ya Nema
- Babu Inda Na Ce Zan Janye Wa Wani Takarata – Atiku
Tawaga daga gwamnatin Jihar Nasarawa karkashin jagorancin Mataimakin Gwamna, Dakta Emmanuel Agbadu Akabe, ta kasance a wurin domin karɓar gawar marigayin.
Haka kuma, an hangi tawagar ƙungiyar yaren marigayin ta Eggon Cultural Development Association (ECDA) da kuma tsohon ɗan takarar gwamna a jam’iyyar PDP, Dakta Emmanuel David Emmanuel (Davematics), a wurin tarbar gawar.