Home » Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Tallafin Biliyan 16

Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Tallafin Biliyan 16

Gidauniyar Aliko Dangote (ADF) ta kaddamar da shirin rabon abinci na kasa na 2025 da darajarsa ta kai Naira biliyan 16, wanda zai tallafawa ‘yan Najeriya miliyan daya da kayan abinci.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Gidauniyar Aliko Dangote (ADF) ta kaddamar da shirin rabon abinci na kasa na 2025 da darajarsa ta kai Naira biliyan 16, wanda zai tallafawa ‘yan Najeriya miliyan daya da kayan abinci.

Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar da aka gudanar a Jihar Kano, Shugaban Gidauniyar, Alhaji Aliko Dangote, wanda diyarsa Maryam Aliko Dangote ta wakilta, ta bayyana cewa shirin yana da burin rage radadin talauci da yunwa a wannnan lokacin.

Wannan shiri yana nuna tausayawa, hadin kai da kuma kishin al’umma. A cikin wannan mawuyacin hali da kasar ke fuskanta, muna kokarin bayar da gudunmuwa domin rage matsin rayuwa,” in ji shi.

Shirin zai fara ne a Jihar Kano, inda za a raba jakunkuna 120,000 na shinkafa ga talakawa a kananan hukumomi 44 na jihar, kafin a ci gaba da rabawa a sauran jihohin Najeriya.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda Mataimakinsa, Comrade Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya wakilta, ya jinjinawa Dangote bisa wannan gagarumin tallafi da ke nufin kawar da yunwa a kasar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?