Gidauniyar Aliko Dangote (ADF) ta kaddamar da shirin rabon abinci na kasa na 2025 da darajarsa ta kai Naira biliyan 16, wanda zai tallafawa ‘yan Najeriya miliyan daya da kayan abinci.
Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar da aka gudanar a Jihar Kano, Shugaban Gidauniyar, Alhaji Aliko Dangote, wanda diyarsa Maryam Aliko Dangote ta wakilta, ta bayyana cewa shirin yana da burin rage radadin talauci da yunwa a wannnan lokacin.
Wannan shiri yana nuna tausayawa, hadin kai da kuma kishin al’umma. A cikin wannan mawuyacin hali da kasar ke fuskanta, muna kokarin bayar da gudunmuwa domin rage matsin rayuwa,” in ji shi.
- Gobara Ta Halaka Mutane 7 Da Lalata Kadarorin N50m A Kano
- Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Ya Ce Yana Nan Daram A APC
Shirin zai fara ne a Jihar Kano, inda za a raba jakunkuna 120,000 na shinkafa ga talakawa a kananan hukumomi 44 na jihar, kafin a ci gaba da rabawa a sauran jihohin Najeriya.
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda Mataimakinsa, Comrade Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya wakilta, ya jinjinawa Dangote bisa wannan gagarumin tallafi da ke nufin kawar da yunwa a kasar.