A safiyar Juma’a, 3 ga oktoba, Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci rantsar da sabon kwamishinan shari’a na jihar, Baristra Abdulkarim Maude SAN, a rukunin gidajen Kwankwasiyya da kw kan titin zuwa Zariya.
A farkon makon nan ne dai aka bai wa Barista Abdulkarim Maude lambar ƙwarewa ta SAN (Senior Advocate of Nigeria) a kotun ƙoli da ke Abuja, babban birnin tarayya.
- Zafi Ya Fasa Tankin Ruwa A Malam Madori, Mutane Da Dama Sun Jikkata
- Ƴan Bindiga Sun Sace Kansiloli Biyu da Limami A Rumfar Shayi A Zamfara
Sabon kwamishinan ya kafa tarihi a jihar Kano, kasancewar shi ne kwamishinan shari’a na farko mai riƙe lambar girmamawa ta SAN.
Da yake jawabi a wajen rantsuwar, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga Barista Abdulkarim Maude ya zama mai gaskiya da rikon amana a dukkanin ayyukan da za a damƙa masa domin amfanin al’ummar Kano.
