ABBA KABIR YUSUF

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Rantsar Da Barista Abdulkarim Maude Kwamishinan Shari’a

A safiyar Juma’a, 3 ga oktoba, Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci rantsar da sabon kwamishinan shari’a na jihar, Baristra Abdulkarim Maude SAN, a rukunin gidajen Kwankwasiyya da kw kan titin zuwa Zariya.

A farkon makon nan ne dai aka bai wa Barista Abdulkarim Maude lambar ƙwarewa ta SAN (Senior Advocate of Nigeria) a kotun ƙoli da ke Abuja, babban birnin tarayya.

Sabon kwamishinan ya kafa tarihi a jihar Kano, kasancewar shi ne kwamishinan shari’a na farko mai riƙe lambar girmamawa ta SAN.

Da yake jawabi a wajen rantsuwar, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga Barista Abdulkarim Maude ya zama mai gaskiya da rikon amana a dukkanin ayyukan da za a damƙa masa domin amfanin al’ummar Kano.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *