Gwamna Uba Sani Ya Dakatar Da Kwamishinan Yada Labaran Gwamnatin Kaduna.

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani , ya dakatar da kwamishinan yada labaran jihar, Muhammad Bello daga kujerarsa.

Babban sakatren yada labaran gwamnan jihar , Ibrahim Musa, ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a jiya Talata.

Sanarwar ta ce gwamnan ya maye gurbinsa da Ahmed Maiyaki, a matsayin sabon kwamishinan yada labaran jihar, nan take.

Post masu alaƙa

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 26 a Borno

Tinubu ya tafi hutun mako uku

Gwamnatin Kwara ta haɗa mutum 146 da aka sace a Woro da iyalansu