Gwamna Uba Sani Ya Dakatar Da Kwamishinan Yada Labaran Gwamnatin Kaduna.

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani , ya dakatar da kwamishinan yada labaran jihar, Muhammad Bello daga kujerarsa.

Babban sakatren yada labaran gwamnan jihar , Ibrahim Musa, ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a jiya Talata.

Sanarwar ta ce gwamnan ya maye gurbinsa da Ahmed Maiyaki, a matsayin sabon kwamishinan yada labaran jihar, nan take.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya