Gwamna Uba Sani Ya Dakatar Da Kwamishinan Yada Labaran Gwamnatin Kaduna.

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani , ya dakatar da kwamishinan yada labaran jihar, Muhammad Bello daga kujerarsa.

Babban sakatren yada labaran gwamnan jihar , Ibrahim Musa, ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a jiya Talata.

Sanarwar ta ce gwamnan ya maye gurbinsa da Ahmed Maiyaki, a matsayin sabon kwamishinan yada labaran jihar, nan take.

Post masu alaƙa

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutuwar wanda ake zargi da sokawa matashi Wuƙa a Kano

Babachir Lawal ya fita daga ADC