Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani , ya dakatar da kwamishinan yada labaran jihar, Muhammad Bello daga kujerarsa.
Babban sakatren yada labaran gwamnan jihar , Ibrahim Musa, ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a jiya Talata.
Sanarwar ta ce gwamnan ya maye gurbinsa da Ahmed Maiyaki, a matsayin sabon kwamishinan yada labaran jihar, nan take.