Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Abdulqadir Mohammed ya sanar da nadin karin wasu mataimaka na siyasa guda 168 da za su taimaka masa wajen tafiyar da jihar.
Wannan na kunshe a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Mukhtar Gidado ya fitar, Gwamna Bala Mohammed ya bayyana sabbin nade-naden mutane 168 da suka hada da manyan mataimaka na musamman, mataimaka na musamman.
Wadanda aka nada sun hada da manyan mataimaka na musamman guda biyar akan harkokin siyasa da al’umma, daya akan al’amuran fansho, mataimaka na musamman 60 da sauransu.
- NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyin Naira Biliyan Daya A Kano Da Legas
- Tsohon Shugaban ‘Immigration’ Ya Ba Tinubu Shawara Kan Sha’anin Tsaro
Gidado ya jaddada cewa an kafin a nadin, an dubi cancanta, ƙwarewa da gogewa, da kuma iya shugabancin waɗanda aka nada, domin da yawa daga cikinsu tsoffin jami’an siyasa ne.
Ya bayyana matakin an gwamnan jihar Bauchi a matsayin wani bangare na dabarun karfafa harkokin mulki, kara kawo hadin kai, da kuma karfafa hanyoyin samun nasarorin gwamnatin a ajihar.