NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyin Naira Biliyan Daya A Kano Da Legas

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Najeriya NDLEA ta sanar da kama miyagun ƙwayoyi da tabar wiwi da kuɗinsu ya haura naira biliyan ɗaya.

Hukumar ta ce ta yi kamen ne a jihohin Legas da Kano da kuma Jigawa, kuma cikin mutanen da aka kama har da wasu mata ‘yan kasar waje uku.

Matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi a Najeriya ta zama ruwan dare, inda masharhanta ke cewa iyaye da al’umma baki daya su hada kai wajen yakar matsalar.

Post masu alaƙa

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 26 a Borno

Tinubu ya tafi hutun mako uku

Gwamnatin Kwara ta haɗa mutum 146 da aka sace a Woro da iyalansu