NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyin Naira Biliyan Daya A Kano Da Legas

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Najeriya NDLEA ta sanar da kama miyagun ƙwayoyi da tabar wiwi da kuɗinsu ya haura naira biliyan ɗaya.

Hukumar ta ce ta yi kamen ne a jihohin Legas da Kano da kuma Jigawa, kuma cikin mutanen da aka kama har da wasu mata ‘yan kasar waje uku.

Matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi a Najeriya ta zama ruwan dare, inda masharhanta ke cewa iyaye da al’umma baki daya su hada kai wajen yakar matsalar.

Post masu alaƙa

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutuwar wanda ake zargi da sokawa matashi Wuƙa a Kano

Babachir Lawal ya fita daga ADC