NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyin Naira Biliyan Daya A Kano Da Legas

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Najeriya NDLEA ta sanar da kama miyagun ƙwayoyi da tabar wiwi da kuɗinsu ya haura naira biliyan ɗaya.

Hukumar ta ce ta yi kamen ne a jihohin Legas da Kano da kuma Jigawa, kuma cikin mutanen da aka kama har da wasu mata ‘yan kasar waje uku.

Matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi a Najeriya ta zama ruwan dare, inda masharhanta ke cewa iyaye da al’umma baki daya su hada kai wajen yakar matsalar.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda