Home » Gwamnatin Kano Za Ta Dasa Bishiyoyi Dubu 10 A Kowace Karamar Hukuma

Gwamnatin Kano Za Ta Dasa Bishiyoyi Dubu 10 A Kowace Karamar Hukuma

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Mataimakin gwamnan Kano Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo ya ce gwamnatinsu za ta dasa bishiyoyi dubu 10 a kananan hukumomi 44 da ke fadin jihar.

Kwamared Aminu ya bayyana hakan ne yayin kaddamar da shirin fara dashen bishiyoyi a fadin kananan hukumomi 44, da aka gudanar a karamar hukumar Tsanyawa.

Ya ce, dasa bishiya sadakace mai saukin aiwatarwa a tsakanin al’umma, saboda haka za a rabawa limamai da Hakimai da Dagataii da masu unguwanni da sauran masu rike da muƙamin gwamnati bishiya guda-guda  su dasa.

Mataimakin gwamnan ya ce, za su sa ido wurin tabbatar da cewa  duk wanda aka bashi bishiya ya kula da ita harta girma.

Ya kuma bayyana dashen bishiyoyin a matsayin wani yunkuri da zai taimaka wajan kare muhalli daga kwararowar hamada da kuma yaki da matsalar dumamar yanayi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?