Home » Hisbah A Jihar Katsina Ta Lalata Barasar Naira Miliyan 60

Hisbah A Jihar Katsina Ta Lalata Barasar Naira Miliyan 60

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Dakarun Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina, sun lalata barasa da ƙwayoyi da ta ƙwace da kuɗinsu ya kai kimanin Naira miliyan 60 a Ƙaramar Hukumar Funtua da ke jihar Katsina.

Dokta Aminu Usman Kwamandan Hisbah na jihar Katsina ne ya sanar da hakan ga Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN).

Dokta Aminu ya ce, hukumar ta ƙwace  giya kwalaye 1,750 da jarkoki 33 da aka sarrafa su a cikin Funtua.

Kwamandan ya jinjina wa ma’aikatan hukumar kan ƙoƙarinsu, ya kuma buƙaci su matsa kaimi wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

Kwamandan na Hisbah a jihar Katsinaa ya roƙi shugabannin Addini a jihar da su tallafa wa hukumar, inda ya ce Hisbah ta kowa ce ba ta da gefe.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?