Home » Gwamnatin Najeriya ta bayyana dalilin da ya sa farashin man fetur ya ki raguwa

Gwamnatin Najeriya ta bayyana dalilin da ya sa farashin man fetur ya ki raguwa

by Hassan Abdu Mai Bulawus
0 comment
Gwamnatin Najeriya ta bayyana dalilin da ya sa farashin man fetur ya ki raguwa

Fadar shugaban kasar Najeriya ta yi bayanin dalilin da yasa farashin man fetur ba zai yi kasa ba.

A wani ƙarin hasken da kakakin shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale ya yi, ya bayyana dangantakar dake tsakanin matatun man fetur da kuma farashinsa, sannan kuma yace farashin man ya dogara ne kacokan akan kuɗin gangar mai a kasuwannin duniya, sai dai, Ngelale ya bayyana cewa akwai amfani mai tarin yawa ga duk ƙasar da ta mallaki matatun man fetur masu aiki.

Ngelale yace farashin man fetur ba zai yi ƙasa a nan Najeriya ba, ko da kuwa dukkanin matatun man fetur ɗinta guda biyar suna aiki tare da samar da wadataccen man fetur.

Kakakin shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale yace ba yawan matatun man fetur ke sa  farashin mai ya yi ƙasa ba, ya ce hakan tatsuniya ce kawai domin babu inda hakan ke faruwa a faɗin duniya.

Kakakin shugaban ƙasar ya bayyana cewa dalilin da ya sanya farashin man fetur ba zai yi ƙasa ba ko da kuwa akwai matatun man fetur shi ne, babu wanda zai kashe dubban miliyoyin kuɗi ya gina matatun mai domin sadaka ko taimakawa al’umma, yace duk wanda ya gina matatun mai yana yi ne kawai don samun riba.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?