Gwamnatin Nijar Ta Rusa Kungiyoyin Kwadago

Gwamnatin mulkin soji a jamhuriyar Nijar ta rusa ƙungiyoyin ƙwadago guda uku da ke wakiltar jami’an tsaro da suka haɗa da na ma’aikatan kwastam da na ma’aikatar kula da ruwa da gandun daji.

Wannan na ƙunshe cikin wata sanarwar da ma’aikatar harkokin cikin gida ta fitar.

Hukumomin sun ɗauki wannan mataki ne kamar yadda kundin tsarin mulkin na 26 ga watan Maris ɗin shekarar nan ya tanada.

Post masu alaƙa

Yan sanda sun kama mutane 79 tare da kwato kwayoyi da makamai a bikin Takutaha a Kano.

Yan sanda sun kama wanda ake zargi da damfarar masu neman aikin gwamnati Naira miliyan 40.

Sabuwar majalisar gudanarwa ta POLAC za ta mayar da hankali kan inganta da ilimi da horo.