Hadarin Jirgin Ruwa: Shugaban Najariya Ya Ba da Umarnin Kai Kayan Agaji Jihar Kwara

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin kai kayan agaji da taimakon da ya wajaba nan take ga mutanen da suka kuɓuta da kuma dangi da iyalan waɗanda suka mutu a hatsarin jirgin ruwan Kwara.

Wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na shugaban ƙasa Abiodun Oladunjoye ya fitar, ta ce, shugaban ƙasa ya nuna takaicin wannan hatsarin jirgin ruwa da ya kashe mutum 150 a jihar ta Kwara.

Ya kuma umarci gwamnatin jihar Kwara da sauran hukumomin gwamnatin tarayya da lamarin ya shafa su yi aiki tare don gano sanadi na kusa da na nesa da suka janyo aukuwar hatsarin jirgin ruwan.

Shugaban ya kuma yi alƙawarin cewa gwamnatinsa za ta yi nazari kan matsalolin sufurin ruwa a ƙasar nan, don tabbatar da ganin ana aiki da matakan kare rayuka da ƙa’idojinsu.

Post masu alaƙa

Kwalejin Fasaha ta Kogi ta dakatar da lakcarori 7 kan cin zarafin ɗalibai

AIG Garba Ahmed ya bukaci daliban Sakandaren ’Yan Sanda Dawakin Kudu su zama jakadu na gari.

Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu sha da dillancin miyagun ƙwayoyi a Kano – Anti-Phone Snatching Force.