Home » Hawan Kilisa A Kano Yanzu Sai Da Izini

Hawan Kilisa A Kano Yanzu Sai Da Izini

by Halima Djimrao
0 comment
Wasu matasa 7 sun shiga komar rundunar 'yan sandan jihar Kano

Rundunar yan sandan jahar Kano ta haramta gudanar da hawan Kilisa, da na angwanci da kuma zaman majalisi har sai an nemi izini daga Fadar Sarkin Kano.

Kwamishinan yan sandan jahar Kano CP Muhammad Usaini Gumel, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da kakakin  rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanya wa hannu.

CP Gumel ya ce sun ɗauki wannan mataki ne sakamakon yadda wasu matasa ke yunƙurin mayar da hannun agogo baya kan abinda ya shafi tsaro a jahar domin sun gano cewa a irin wuraren ake  aikata laifuka.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?