• Home  
  • Hukumar Hisba Ta Gana da ‘Yan TikTok
- Labarai

Hukumar Hisba Ta Gana da ‘Yan TikTok

A yau ne hukumar Hisba ta Kano, ƙarƙashin jagorancin Kwamandanta, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ta gana da ‘Yan TikTok a hedkwatar hukumar da ke Sharaɗa.

HizbaKano

A yau ne hukumar Hisba ta Kano, ƙarƙashin jagorancin Kwamandanta, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ta gana da ‘Yan TikTok a hedkwatar hukumar da ke Sharaɗa.

An shirya ganawar ne domin a sami kyakkyawar jituwa tsakaninsu da Hukumar Hisba, don ƙara inganta tarbiyyarsu.

A yayin ganawar, Daurawa ya yi wa ‘Yan Tiktok ɗin alƙawuran da suka haɗa da ba su jari da aurar da su, har ma da mayar da wasu daga cikinsu makaranta.

A karshe kuma kwamandan ya raba wa kowannensu Naira 2000 a matsayin kuɗin data da kuma na mota.

Manya ‘Yan rawar TikTok ɗin da dama sun samu halartar taron.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai