INEC ta kai wa CBN ajiyar muhimman kayan zaɓen Gwamnan Osun

A yayin da ake shirin gudanar da zaɓen Gwamnan Jihar Osun a ranar Asabar, muhimman kayan aikin da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) za ta yi amfani da su wajen gudanar da zaɓe sun isa Jihar.

INEC ta sauke muhimman kayan zaɓen ne a Babban Bankin Najeriya (CBN) reshen Osogbo, babban birnin jihar, kafin raba su a yau Juma’a gabanin zaɓen da zai gudana a ranar Asabar ɗin nan.

 

Post masu alaƙa

Hisbah za ta fara farautar masu aikata baɗala a Kano

Kwastam ta kama harsasai 3,300 da kayayyakin fasa-ƙwauri a Seme

Jigawa na da ƙarfin samar da sama da kashi 50 cikin 100 na buƙatar shinkafar Najeriya – Shugaban NUJ