Home » Iran Ta Harba Makamai Masu Linzami 100 Isra’ila, Mutane 40 Sun Jikkata

Iran Ta Harba Makamai Masu Linzami 100 Isra’ila, Mutane 40 Sun Jikkata

IDF, Avichay Adraee mai magana da yawun rudunar sojin Isra'ila ya ce Iran ta harbo wa ƙasar su aƙalla makamai masu linzami 100. 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

IDF, Avichay Adraee mai magana da yawun rudunar sojin Isra’ila ya ce Iran ta harbo wa ƙasar su aƙalla makamai masu linzami 100. 

Adraee ya bayyana hakan ne a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce an kakkaɓo akasarin makaman da ƙasar Iran ta harbo musu.

Ya ƙara da cewa wasu daga cikin makaman da aka harbo basu samu isa wuraren da aka so ace sun kai ba.

Hukumomi a fannin kiwon lafiya na Isra’ila sun ce mutane 40 ne harin ya shafa wanda a yanzu suke karɓar kulawa a asibitoci daban daban, kuma biyu daga ciki na cikin mawuyacin hali. Kamar yadda kafar yaɗa labarai ta BBC Hausa ta wallafa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?