Iran Ta Harba Makamai Masu Linzami 100 Isra’ila, Mutane 40 Sun Jikkata

IDF, Avichay Adraee mai magana da yawun rudunar sojin Isra’ila ya ce Iran ta harbo wa ƙasar su aƙalla makamai masu linzami 100. 

Adraee ya bayyana hakan ne a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce an kakkaɓo akasarin makaman da ƙasar Iran ta harbo musu.

Ya ƙara da cewa wasu daga cikin makaman da aka harbo basu samu isa wuraren da aka so ace sun kai ba.

Hukumomi a fannin kiwon lafiya na Isra’ila sun ce mutane 40 ne harin ya shafa wanda a yanzu suke karɓar kulawa a asibitoci daban daban, kuma biyu daga ciki na cikin mawuyacin hali. Kamar yadda kafar yaɗa labarai ta BBC Hausa ta wallafa.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda