Home » Iran Ta Karrama Kwamandanta Da Ya Kai Hari Isra’ila 

Iran Ta Karrama Kwamandanta Da Ya Kai Hari Isra’ila 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Ayatullah Khamenei Jagoran Musulunci na ƙasar Iran, ya karrama kwamandan dakarun kare juyin juya hali da ya jagoranci harin makami mai linzami da ƙasar ta kai wa Isra’ila a ranar Talatar makon jiya.

Ayatullah Khamenei ya sanya wa Janar Amirali Hajizadeh aninin Fath (nasara), a ranar Lahadi da ta gabata.

Karramawar ga Janar Amirali Hajizadeh ta zo ne saboda “kyakkyawan aiki na ‘Gaskiya’”, kamar yadda shafin rundunar juyin juya halin Musulunci na Iran ta bayyana.

Janar Hajizadeh, mai shekaru 62, ya shugabanci sashin kula da sararin samaniyar rundunar sojojin Iran tun lokacin da aka ƙirƙiro ta a shekarar 2009.

Ranar Talatar da ta gabata ce dai rundunar ta harba wasu makamai masu linzami kimanin 200 kan ƙasar Isra’ila a matsayin ramuwar gayya kan harin da Isra’ila ta kai ta sama da ta yi ajalin shugaban kungiyar Hizbullah Sayyid Hassan Nasrallah.

Wannan hari ne kuma ya yi ajalin Janar Abbas Nilforoushan, a Beirut babban birnin ƙasar Lebanon.

Wannan dai shi ne hari na biyu da ƙasar Iran ta kai wa Isra’ila kai tsaye cikin watanni shida.

Ƙasar Isra’ila ta sha alwashin mayar da martani bayan harin makami mai linzami da Iran ta kai mata a ranar Talatar da ta gabata.

 

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?