ISWAP ta kashe kwamandan sojan Najeriya a Borno

Mayaƙan ƙungiyar ISWAP da ke kai hare-hare a jihar Borno sun kashe wani kwamandan sojin saman Najeriya, bayan samun damar katse bayanan wurin da sojojin suke a tsakanin Damboa da Biyu da jihar.

Jaridar PR Nigeria ta rawaito cewa sojan shi ne kwamandan da ke jagorantar rundunar da ta kai wa sojojin haɗin gwiwa na CJTF ɗauki waɗanda ƙungiyar ta yi wa kwantan ɓauna.

Da farko dai sai da kwamandan wanda aka ɓoye sunansa ya wallafa wani bidiyo inda yake sanar da manyansa irin nasarar da suke samu. Sai dai rahotanni sun ce ƴan ƙungiyar sun bibiyi wurin da kwamandan yake sannan suka katse sadarwar, inda kuma suka samu suka kama shi sannan suka kashe shi bayan yi masa tambayoyi.

Kwandan dai na jagorantar rundunar da ke kai ɗauki ga wasu dakarun Najeriya da suka yi ɓatan hanya abin da ya janyo mayaƙan na ISWAP suka yi musu kwantan ɓauna.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda