• Home  
  • Jamhuriyar Nijar Ta Fice Daga Kawancen Yakar ‘Yan Ta’addan Boko Haram
- Babban Labari - Labarai

Jamhuriyar Nijar Ta Fice Daga Kawancen Yakar ‘Yan Ta’addan Boko Haram

Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar karkashin jagorancin Janar Abdurrahmane Tchiane ta bayyana janye dakarunta daga rundunar Hadin Gwiwa mai yaki da Boko Haram a yankin Tafkin Chadi.

Ƙasashen Mali da Burkina Faso da kuma Guinea, sun bayyana cewa duk wani yunƙurin yin amfani da ƙarfin soja don dawo da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Nijar Mohamed Bazoum tamkar ƙaddamar da yaƙi ne a kansu.
Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar karkashin jagorancin Janar Abdurrahmane Tchiane ta bayyana janye dakarunta daga rundunar Hadin Gwiwa mai yaki da Boko Haram a yankin Tafkin Chadi.
Gwamnatin ta ce ta  janye dakarun nata ne domin mayar da hankali wajen tabbatar da tsaron bututun mai na ƙasar da ke fuskantar hare-haren ƴan bindiga.
Wannan mataki na gwamnatin jamhuriyar Nijar ya zo wa mutane da dama da fuskoki daban daban inda wasu ke ganin an yi dai dai, wasu kuma ke ganin akasin haka.
A baya bayan nan ne dai aka tabbatar wa Janar Abdurrahmane Tchiane wa’adin mulki na shekara biyar, inda ake sa ran kafin wannan lokacin, zai inganta rayuwar kasar da ‘ya’yanta.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai