Jigawa: Hukumomin Shari’a Sun Sallami Wani Alƙali Saboda Karɓar Rashawa

Hukumar shari’a ta jahar Jigawa ta kori wani Alƙalin kotun shari’ar addinin musulinci a Birnin Kudu ,mai shari’a Safiyanu Muhammad Dabi, bisa laifin karɓar cin hancin naira dubu Hamsin (50,000) daga hannun wani mai ƙara.

Bayanin hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan yaɗa Labarai kan harkokin shari’a na jahar , Abbas Rufa’i Wangara ya sanya wa hannu tare da rabawa manema labarai a birnin Dutse babban birnin jahar Jigawa.

Wangara Ya kara cewa Alƙalin ya karɓi kuɗi naira dubu 50,000 ne a matsayin cin hanci a lokacin da wanda ake ƙara ya bayyana a gaban Alƙalin.

Sanarwar ta ƙara da cewa, biyo bayan tattaunarwa mai zurfi da hukumar kula da harkokin shari’a , a taron ta karo na 170 ne ta yanke shawarar dakatar da Alƙalin.Kazalika hukumar ta gargaɗi ma’aikatan ta da su guji duk wani nau’in cin hanci da rashawa.

Post masu alaƙa

Kotun majistare ta fara sauraren shari’ar sojan gona mai mukamin CSP 

Rundunar yan sandan jihar Kano ta kama wanda ake zargi da damfarar mutane da cewa shi babban jami’in Dan sandan ne.

Hisbah ta fara horas da sabbin jami’anta a Jigawa