Home » Kano: sabon sakataren zartarwa na hukumar alhazai ya kama aiki

Kano: sabon sakataren zartarwa na hukumar alhazai ya kama aiki

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Kano: sabon sakataren zartarwa na hukumar alhazai ya kama aiki

Sabon Sakataren zartarwar na hukumar jin dadin alhazai ta jihar kano, Alhaji Lamin Rabi’u ya kama aiki a yau din nan bayan nada shi da sabon gwamnan jihar kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi.

Yayin da yake jawabi Sakataren zartarwar ya godewa Allah subhanahu wata’allah bisa yadda ya baiwa gwamnan Kano ikon Mayar da shi hukumar domin sake hidimtawa alhazai bakin Allah.

Lamin Rabi’u ya kuma bada tabbacin zai yi duk mai yiyuwa wajen wajen ganin an sami nasarar gudanar da ibadar aikin hajjin bana, Inda ya bukaci alhazan da su bada hadin kai don kyautata musu tun daga nan Kano har zuwa can kasa mai tsarki.

Rhotanni sun tabbatar da cewa wannan ne karo na uku da Alhaji Lamin Rabi’u ya sake komawa hukumar a matsayin Sakataren zartarwa na hukumar jin dadin alhazai ta jihar kano.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?