Kasashen Mali da Burkina Faso za su aike da tawaga kasar Nijar

Ƙasar Mali ta ce za ta tura tawagar haɗin guiwa da Burkina Faso domin jaddada goyon bayan su ga sojojin da suka yi juyin mulki a ƙasar.

Sanarwa na zuwa ne bayan da shuwagabannin soji na ƙasar Nijar suka yi watsi da umarnin ƙungiyar na mayar da mulki ga hamɓararren shugaban.

Sojojin Nijar sun sanar da rufe sararin samaniyarsu da iyakokin ƙasar, sun kuma ce a shirye suke wajen kare ƙasarsu.

Kawunan ƙasashen ƙungiyar ya rabu kan ɗauka matakin soji a kan Nijar.

Najeriya da Ivory Coast na kan gaba wajen jaddada buƙatar mayar da shugaba Bazoum bisa shugabancin ƙasar.

Sai dai shugabannin mulkin soji na ƙasashen Mali da Burkina Faso sun nuna goyon bayan su ga Sojojin Nijar, sun kuma ce zasu shigar masu faɗa madamar Ecowas ta kai ma Nijar hari.

Post masu alaƙa

AIG Garba Ahmed ya bukaci daliban Sakandaren ’Yan Sanda Dawakin Kudu su zama jakadu na gari.

Venezuela ta sanar da ficewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya

Babu ɗaga ƙafa tsakanin mu da masu sha da dillancin miyagun ƙwayoyi a Kano – Anti-Phone Snatching Force.