Dan majalisar wakilai, Bello El-Rufai, dan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa Kotun Tarayya da ke jihar ta bayar da belin mahaifinsa.
Daily Trust ta rawaito cewa a cewar dan majalisar, wanda ke cikin kotun lokacin zaman yayin da aka hana ‘yan jarida shiga, su na ƙoƙarin cika sharuddan belin da kotun ta gindaya.
Haka kuma, wani jigo a jam’iyyar ADC kuma na hannun daman El-Rufai, Hayatudeen Lawal Makarfi, ya tabbatar da batun, inda ya ce an daura wasu sharudda kan belin.
Ya kuma nuna kwarin gwiwar cewa za a cika sharuddan nan ba da jimawa ba.
Tun da fari Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta gurfanar da El-Rufai a kotun jihar Kaduna, inda aka dage sauraron bukatar belin zuwa ranar 21 ga watan Afrilu, 2026.