Kotu ta ba belin mahaifi na – Bello El-Rufai

Dan majalisar wakilai, Bello El-Rufai, dan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa Kotun Tarayya da ke jihar ta bayar da belin mahaifinsa.
Daily Trust ta rawaito cewa a cewar dan majalisar, wanda ke cikin kotun lokacin zaman yayin da aka hana ‘yan jarida shiga, su na ƙoƙarin cika sharuddan belin da kotun ta gindaya.
Haka kuma, wani jigo a jam’iyyar ADC kuma na hannun daman El-Rufai, Hayatudeen Lawal Makarfi, ya tabbatar da batun, inda ya ce an daura wasu sharudda kan belin.
Ya kuma nuna kwarin gwiwar cewa za a cika sharuddan nan ba da jimawa ba.
Tun da fari Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta gurfanar da El-Rufai a kotun jihar Kaduna, inda aka dage sauraron bukatar belin zuwa ranar 21 ga watan Afrilu, 2026.

Post masu alaƙa

Kotun ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar ADC

Babu wata kotu da ta wanke Murtala Sule Garko daga zargin badaƙalar kudi – Baba Jibo

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta raba Naira miliyan ɗaya ga matasa 36 a shirin haɗin gwiwa na magance aikata laifuka