’Yansanda sun kama mutane 193 tare da kwato makamai da kwayoyi a Kano

Rundunar ’yansandan Najeriya a jihar Kano ta kai samame wuraren da ake zargin maboyar masu aikata laifuka ne, inda ta kama mutane 193 tare da kwato makamai masu haɗari da kuma miyagun ƙwayoyi.
Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar a jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar.
A cewar sanarwar, daga cikin kayan da aka kwato akwai adduna, wuƙaƙe, goraye, da kuma miyagun ƙwayoyi irin su Pregabalin da tabar wiwi.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ibrahim Bakori, ya bayyana cewa wannan samame na daga cikin matakan da rundunar ke ɗauka domin ƙarfafa tsaro da rage yawaitar laifuka a faɗin jihar, yana mai cewa bincike kan lamarin na ci gaba.
Rundunar ta kuma yaba wa jami’anta bisa ƙwazo da jajircewa, tare da gode wa al’umma kan haɗin kai da suke bayarwa. Haka zalika, ta buƙaci mazauna jihar da su riƙa kai rahoton duk wani abu da suke zargi ga hukumomi domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro.

Post masu alaƙa

Kotun ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar jam’iyyar ADC

Babu wata kotu da ta wanke Murtala Sule Garko daga zargin badaƙalar kudi – Baba Jibo

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta raba Naira miliyan ɗaya ga matasa 36 a shirin haɗin gwiwa na magance aikata laifuka