Kotu ta hana a yi belin Abubakar Malami

Wata babbar kotun tarayya a Abuja ta yi watsi da buƙatar neman beli da tsohon ministan Shari’ar Najeriya, Abubakar Malami ya yi domin sakin sa daga hannun hukumar EFCC.

Mai Shari’a Babangida Hassan ya ce bai zai iya amince wa da buƙatar belin ba saboda doka ta bai wa hukumar EFCC ta tsare tsohon ministan shari’ar domin ci gaba da bincike.

Tun dai ranar 8 ga watan Disamba Abubakar Malami ke tsare a wurin hukumar ta EFCC.

A ranar Laraba ne Malami ya kwarmata cewa jami’an hukumar sun kai samame ofishinsa da gidajensa da ke Abuja da Kebbi.

EFCC na riƙe da malami ne kan tuhumar laifuka guda uku waɗanda tsohon ministan ya musanta.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda