Kotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yari

Wata babbar kotun tarayya mai zamanta a garin Gwarimpa da ke babban birnin tarayya Abuja ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige a gidan yarin Kuje.

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC ce ta gurfanar da tsohon ministan a gaban mai shari’a Mariam Hassan bisa tuhume-tuhume guda takwas da suka danganci cin hanci da rashawa.

Ngige, wanda ya kasance minista a zamanin mulkin tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya isa harabar kotun ne da misalin ƙarfe 8:10 na safiyar yau Juma’a tare da rakiyar jami’an EFCC.

Hukumar ta zargi Ngige da aikata laifukan ne a lokacin da yake minista, musamman a lokacin da yake kula da hukumar bayar da tallafi ta Najeriya wato NSITF.

A tuhuma ta farko, ana zargin cewa daga Satumban 2015 zuwa Mayun 2023, Ngige ya yi amfani da matsayinsa a lokacin matsayin tsohon minista wajen bai wa abokansa cin gajiyar kwangila ba bisa ka’ida.

Sai dai a zaman kotun, tsohon ministan ya musanta laifukan da ake tuhumarsa da su.

Mai shari’a Mariam ta ɗage shari’ar zuwa Litinin domin sauraron buƙatar neman belinsa, sannan ta bayar da umarni a tsare shi a gidan yarin Kuje har zuwa ranar.

Post masu alaƙa

Rukunin farko na ‘yan Najeriya da aka kwashe daga Afirka ta Kudu zai isa ƙasar ranar Alhamis

Gwamnatin Sakkwato ta tallafa wa Alhazai 47 da suka ɓatar da kuɗin guzurinsu

An kammala shirye-shiryen tabbatar da tsaro a zaɓen cike gurbin ɗan majalissar wakilan Dawakin Kudu/Warawa a Kano.