Home » Kotu Ta Umarci Rundunar Yan Sanda Ta Kasa Ta Binciki Abdullahi Abbas Da Fa’izu Alfindiki Kan Zargin Bata Sunan Gwamnan Kano

Kotu Ta Umarci Rundunar Yan Sanda Ta Kasa Ta Binciki Abdullahi Abbas Da Fa’izu Alfindiki Kan Zargin Bata Sunan Gwamnan Kano

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

 

Babbar kotun shari’ar musulunci dake zamanta a kasuwar kurmi Kano, ta bai wa mataimakin babban Sufetan ƴan sandan Nijeriya mai kula da shiyya ta ɗaya,  ya binciki shugaban jam’iyar APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas da kuma tsohon shugaban karamar hukumar Birnin Kano, Faizu Alfindiki, kan zarginsu da  ɓata wa Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf suna.

Tun da fari dai Hon. Amir Abdullahi Kima, mai taimakawa gwamnan Kano a Ma’aikatar Shari’a da kuma  Ishak Abdul Mataimakin Gwamnan kan fasahar zamani ne suka yi ƙararsu a kotun ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Abdu Abdullahi Wayya.

Kotun Kuma ta aike musu da sammaci amma wadanda ake karar basu bayyana ba, daga bisani suka turo lauyoyinsu tare da bayanin sukar hurumin kotu.

A zaman kotun na ranar Alhamis Mai Shari’ar ya tabbatar da hurumin kotun akan shariar, ya kuma umarci Ofishin ƴan sanda na  shiya ta daya wato Zone One dake Kano kan su binciki waɗanda ake zargin, sannan su kawo su kotun domin fuskantar shari’ar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?