Lakurawa Sun Tada Bam A Zamfara- Police 

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce kungiyar ‘yan ta’addar Lakurawa ne suka tayar da bama-bamai a wasu kauyuka biyu na gundumar Dansadau a karamar hukumar Maru.  

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara CP Muhammad Shehu Dalijan ne ya bayyana hakan a wata zantawa da manema labarai ta wayar tarho.

CP Muhammad ya tabbatar da tashin bama-baman a kauyen ‘Yar Tasha da ke kan hanyar Dansadau.

Kwamishinan ya ce tashin bama-baman ya yi sanadaiyyar mutuwar mutum daya, yayin da wasu uku suka samu raunuka daban-daban.

An ce bama-baman da ake zargin ‘yan ƙungiyar ta’addar Lakurawa da dasa wa sun tashi da misalin karfe 8 na safiyar ranar Laraba.

Post masu alaƙa

Kwamitin zaman lafiya ya gana da yan sandan Kano kan zaɓen 2027.

An kashe kwamandojin ’yan bindiga biyu a Katsina

NAPTIP ta ceto sama da yara 180 da ake safararsu ta hanyar ƙungiyoyin fara hula na bogi