Home » Ma’aikatan Da Ba Za A Biya Albashin Dubu 70 Ba

Ma’aikatan Da Ba Za A Biya Albashin Dubu 70 Ba

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Karamin sashe na ɗaya na babban sashe na huɗu na dokar albashin Najeriya na 2019 da aka yi wa kwaskarima a 2024 ya ce biyan albashi mafi ƙaranci na naira dubu 70 bai shafi wasu ma’aikatu ba. 

Sashen ya lissafo su kamar haka:

Ma’aikatun da ke da ma’aikatan wucin-gadi.

Dillalai, waɗanda ma’aikatu ke biyan su daidai da aikin da suke yi a wani ƙayyadadden lokaci.

Ma’aikatun da masu yi musu aiki ba su kai mutane 25 ba.

Ma’aikatan da ke aiki na lokaci zuwa lokaci kamar masu aikin ƙwadago a ma’aikatu ko gona.

Ma’aikatan jirgin sama ko na ruwa waɗanda dokokin aikinsu suka bambamta da sauran ka’idojin ayyuka.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?