Home » Majalisar Shari’ar Musulunci Ta Bukaci Matasa Su Nisanci Zanga-Zanga

Majalisar Shari’ar Musulunci Ta Bukaci Matasa Su Nisanci Zanga-Zanga

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Majalisar Koli ta Shari’ar Musulunci ta Najeriya ta bukaci matasa su nisanci zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a fadin kasar.

Shehu Muhammad Makarfi da ya wakilci majalisar a wajen taron bita na kwanaki biyu da Kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI) ta shirya mai taken “Dogaro da Kai da Kame Kai: Mafi Girman Dabara ga Malamai a cikin Da’awa” a Gombe ne ya bayyana hakan.

Makarfi ya ce duk wanda ke karfafa wa matasan Najeriya guiwa su yi zanga-zanga, ba ya neman maslaha ga kasa.

Ya ce, “Zanga-zanga koma-baya ce ga Najeriya, musamman a Arewaci inda muke jin dadin zaman lafiya.

Shehin malamin ya jaddada bukatar kauracewa zanga-zangar in da ya ce “Ba za mu bari bata-gari su tarwatsa zaman lafiyarmu ba,” ya jaddada.

Ya yi kira ga Gwamnan Jihar Gombe, a matsayin Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, da ya dauki matakai don hada malamai da sarakuna wajen karfafa zaman lafiya da yi wa jama’a gargadi kan hadarin zanga-zanga.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?