• Home  
  • Majalisar Shari’ar Musulunci Ta Bukaci Matasa Su Nisanci Zanga-Zanga
- Babban Labari - Labarai

Majalisar Shari’ar Musulunci Ta Bukaci Matasa Su Nisanci Zanga-Zanga

Majalisar Koli ta Shari’ar Musulunci ta Najeriya ta bukaci matasa su nisanci zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a fadin kasar.

Majalisar Koli ta Shari’ar Musulunci ta Najeriya ta bukaci matasa su nisanci zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a fadin kasar.

Shehu Muhammad Makarfi da ya wakilci majalisar a wajen taron bita na kwanaki biyu da Kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI) ta shirya mai taken “Dogaro da Kai da Kame Kai: Mafi Girman Dabara ga Malamai a cikin Da’awa” a Gombe ne ya bayyana hakan.

Makarfi ya ce duk wanda ke karfafa wa matasan Najeriya guiwa su yi zanga-zanga, ba ya neman maslaha ga kasa.

Ya ce, “Zanga-zanga koma-baya ce ga Najeriya, musamman a Arewaci inda muke jin dadin zaman lafiya.

Shehin malamin ya jaddada bukatar kauracewa zanga-zangar in da ya ce “Ba za mu bari bata-gari su tarwatsa zaman lafiyarmu ba,” ya jaddada.

Ya yi kira ga Gwamnan Jihar Gombe, a matsayin Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, da ya dauki matakai don hada malamai da sarakuna wajen karfafa zaman lafiya da yi wa jama’a gargadi kan hadarin zanga-zanga.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai