Home » Ma’aikatan VOA Sun Maka Shugaba Trump A Kotu

Ma’aikatan VOA Sun Maka Shugaba Trump A Kotu

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Wasu daga cikin ma’aikatan kafar yaɗa labaran Muryar Amurka (VOA), sun maka shugaba Donald Trump, a gaban Kotu bisa zargin sa da rufe kafar yaɗa labaran ba bisa ƙa’ida ba.

Ma’aikatan sun kai ƙarar ne a kotun tarayya da ke Manhattan ne, inda suka zargi Shugaban Amurka Donald Trump, da babbar mai ba shi shawara, Kari Lake, da take haƙƙinsu ta hanyar rufe kafar babu zato ba tsammani, lamarin da ya saɓa wa dokar ƙasar.

Masu shigar da ƙarar su kimanin shida (6), ciki har da tsohon shugaban ofishin White House na VOA, Patsy Widakuswara, da Editar Press Freedom, Jessica Jerreat, suna neman a mayar da ma’aikatan fiye da 900 da kuma na wucin gadi 550 bakin aikinsu.

Sai dai da take kare matakin, Kari Lake, ta ce ma’aikatar tana fama da ɓarna da cin hanci, adan haka bai dace kuɗin harajin Amurkawa su ci-gaba da ɗaukar nauyinta ba, kamar yadda kafar yaɗa NPR ta rawaito.

Tunda bayan rufe kafar yaɗa labaran ta VOA, dukkan shafin yanar gizon ta ya kasance ɗauke da tsaffin labarai, baya ga yadda aka daina kama su ta hanyar da ake samun su kai tsare (live streaming).

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?