• Home  
  • Mahaifiyar Rarara Ta Shaki Iskar ‘Yanci
- Babban Labari

Mahaifiyar Rarara Ta Shaki Iskar ‘Yanci

An sace mahaifiyar Rarara ne a kauyen Kahutu da ke karamar Hukumar Danja da ke JIhar Katsina a karshen watan Yunin 2024

Mahaifiyar shahararren mawaƙin siyasa a Najeriya Dauda Adamu Kahutu Rarara, ta shaki iskar ‘yanci tun bayan da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da ita a karshen watan jiya. 

Mawaƙinne ya sanar da hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Instagram da safiyar ranar Laraba.

Rarara ya ce “Cikin yarda da amincin Ubangiji, mun samu dawowar Mama cikin aminci,”.

A baya dai ‘yan bindigar da suka sace Hajiya Halima Adamu ƙauyen Kahutu da ke ƙaramar hukumar Ɗanja sun bukaci a biya naira miliyan 900 a matsayin kuɗin fansa.

Kawo yanzu  Rarara bai yi ƙarin bayani ba kan ko sai da aka biya kuɗin fansa kafin sakin mahaifiyar tasa.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000