Home » Majalisa Ta Amince Da Dakatar Da Fubara

Majalisa Ta Amince Da Dakatar Da Fubara

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Majalisar Wakilan Najeriya ta amince da dokar ta baci, da kuma dakatarwar da shugaba Tinubu ya yi wa gwamanan jihar Ribas Siminalayi Fubara cikin yanayi na kusan na bai daya.

Wannan ya gudana ne da ranar Alhamis 20/Maris/2025 yayin zaman majalisar, karkashin jagorancin Honarabul Tajuddin Abbas.

Sai dai tuni masana masu sharhi akan dokoki suka far yin tir da abin da ya faru, inda sananne daga cikin ‘yan rajin kare hakkin bil Adama a Najeriya Barr Abba Hikima ya bayyana hakan a matsayin rashin kasar ma baki daya in da ya ce “Ba kasa fa jama’a”.

Tuni dai rahotanni suka tabbatar da cewa sojoji sun karbe ikon gudanarwa a jihar Ribas, inda za su kwashe watanni shida suna gudanar da harkokin jihar kamar yadda shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ayyana.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?