• Home  
  • Majalisa Za Ta Yi Zaman Gaggawa Saboda Zanga-zanga
- Babban Labari - Labarai

Majalisa Za Ta Yi Zaman Gaggawa Saboda Zanga-zanga

Majalisar wakilan Najeriya za ta yi zaman gaggawa ranar Laraba, 31 ga Yuli, 2024 domin shawo kan masu zanga-zanga.

Tajuddeen Abbas

Majalisar wakilan Najeriya za ta yi zaman gaggawa ranar Laraba, 31 ga Yuli, 2024 domin shawo kan masu zanga-zanga.

Hakan na kunshe ne a cikin wata takarda da manema labarai suka yi ido hudu da ita wadda magatakardan majalisar Dokta Yahaya Danzaria ya sanyawa hannu.

Dokta Yahaya Danzaria ya ce, “Bisa umarnin Kakakin majalisar, Honarabul. Abbas Tajudeen, PhD, ya ce a sanar da ku cewa za a yi zaman majalisa ranar Laraba 31 ga Yuli, 2024.

“Yana rokon ku, ku yi shirye-shiryen da suka dace don halartar taron, saboda za a tattauna muhimman batutuwa a wannan zama.

A farkon makon da ya gabata Ƴan Majalisar suka tafi hutu har zuwa ranar 17 ga Satumba, 2024.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai