Home » Majalisa Za Ta Yi Zaman Gaggawa Saboda Zanga-zanga

Majalisa Za Ta Yi Zaman Gaggawa Saboda Zanga-zanga

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Tajuddeen Abbas

Majalisar wakilan Najeriya za ta yi zaman gaggawa ranar Laraba, 31 ga Yuli, 2024 domin shawo kan masu zanga-zanga.

Hakan na kunshe ne a cikin wata takarda da manema labarai suka yi ido hudu da ita wadda magatakardan majalisar Dokta Yahaya Danzaria ya sanyawa hannu.

Dokta Yahaya Danzaria ya ce, “Bisa umarnin Kakakin majalisar, Honarabul. Abbas Tajudeen, PhD, ya ce a sanar da ku cewa za a yi zaman majalisa ranar Laraba 31 ga Yuli, 2024.

“Yana rokon ku, ku yi shirye-shiryen da suka dace don halartar taron, saboda za a tattauna muhimman batutuwa a wannan zama.

A farkon makon da ya gabata Ƴan Majalisar suka tafi hutu har zuwa ranar 17 ga Satumba, 2024.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?