Majalisar dokokin Kano ta gabatar da ƙudurin tsige mataimakin gwamnan Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta fara shirin tsige mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdulsalam, bisa wasu zarge-zarge da aka gabatar a kansa a gaban majalisar, ranar Alhamis.

Shugaban masu rinjaye na majalisar Lawal Hussaini ne ya gabatar da ƙudurin tsige mataimakin gwamnan kan zarge-zarge da suka haɗa da almundahana da kuɗin gwamnati a lokacin da ya shugabanci wasu hukumomin gwamnati.

A kan haka ne majalisar ta ce, kamar yadda doka ta tanada, ta yanke shawarar sanar da mataimakin gwamnan game da matakin da ta fara ɗauka na tsige shi.

A watan Janairu ne gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya sanar da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki a matakin tarayya, daga jam’iyyar NNPP, wadda ya lashe zaɓe ƙarƙashin ta a shekarar 2023.

Sai dai mataimakin nasa Aminu Abdulsalam bai bi shi zuwa jam’iyyar ta APC ba.

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun daƙile yunƙurin garkuwa da mutane tare da ceto mutum 23

Dan KAROTA da direba ya buge ya gudu Nasiru Abdullahi Mai Jihadi ya rasu ya bar mata 2 da ‘ya’ya 12.

An kama budurwa ‘yar shekara 15 kan safarar miyagun kwayoyi a Delta.