Majalisar dokokin Kano ta gabatar da ƙudurin tsige mataimakin gwamnan Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta fara shirin tsige mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdulsalam, bisa wasu zarge-zarge da aka gabatar a kansa a gaban majalisar, ranar Alhamis.

Shugaban masu rinjaye na majalisar Lawal Hussaini ne ya gabatar da ƙudurin tsige mataimakin gwamnan kan zarge-zarge da suka haɗa da almundahana da kuɗin gwamnati a lokacin da ya shugabanci wasu hukumomin gwamnati.

A kan haka ne majalisar ta ce, kamar yadda doka ta tanada, ta yanke shawarar sanar da mataimakin gwamnan game da matakin da ta fara ɗauka na tsige shi.

A watan Janairu ne gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya sanar da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki a matakin tarayya, daga jam’iyyar NNPP, wadda ya lashe zaɓe ƙarƙashin ta a shekarar 2023.

Sai dai mataimakin nasa Aminu Abdulsalam bai bi shi zuwa jam’iyyar ta APC ba.

Post masu alaƙa

Ƴan sandan Kano za su ƙara ƙaimi wajen amsa kiran gaggawa – CP Bakori

Masu Garkuwa Da Janar Rabe Na Neman A Sako ’Yan Bindigar Da Ke Hannun Gwamnati

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu