Home » Majalisa Wakilai Na Son A Tilasta Wa Yan Nijeriya Yin Zaɓe

Majalisa Wakilai Na Son A Tilasta Wa Yan Nijeriya Yin Zaɓe

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

A Najeriya ‘yan majalisar dokokin ƙasar sun sake zama inda suka yi karatu na biyu ga ƙudurin dokar nan da ke neman yin gyaran fuska ga dokar zaɓe ta 2022 da za ta tilasta ‘yan ƙasar jefa ƙuri’a a lokacin manya da ƙananan zaɓuka masu zuwa.

Wannan sabon ƙudurin doka dai ya janyo rarrabuwar kai a majalisar dokokin Najeriyar.

Yayin da wasu ƴan majalisar ke ganin zai zama tamkar take ‘yancin ‘yan ƙasar ne, wasu kuwa na bayyana shi a matsayin mataki mai kyau, wanda idan ya zama doka za a iya cin tara ko kuma yanke masa hukuncin zaman gidan kaso duk wanda ya ƙi yin zaɓe.

‘Yan majalisar dokokin sun gudanar da muhawara tare da tattaunawa game da shirin yin gyaran fuska ga dokar shekarar 2022 da ta shafi zabe domin tabbatar da kowane dan Najeriya ya sauke nauyin da ke kansa na yin zabe.

Sun bayyana cewa akwai bukatar cin tarar naira dubu 100 ga duk wanda ya ki jefa kuri’a ko kuma dauri a gidan yari nana tsawon watanni shidda ko ma duka biyu.

‘Ƴan majalisar dai sun kai ga yi wa kudurin karatu na farko da na biyu, da kakakin majalisar wakilan kasar Tajudeen Abbas ya jagoranci zaman.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?