Matasa Sun Kaddamar Da Zanga-Zanga A Jihar Neja

Masu zanga-zanga a Neja

Matasa a Jihar Neja sun kaddamar da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya.

Masu zanga-zangar sun fantsama kan manyan titunan jihar, ciki har da babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna.

Matasan da ke tafe suna rera wakar adawa da tsare-tsaren gwamnati sun daga kwalaye masu dauke da rubutu a jikinsu da ke nuna bacin ransu kan halin tsadar rayuwa a Najeriya.

A jikin kwalayen sun yi rubuce-rubuce da dama, da suka hada da, ‘A soke tsare-tsere masu kuntata wa jama’a; ‘tura ta kai bango’; ’ ‘Mu Ba Bayi Ba Ne A kasarmu’; ‘Ba Za Mu Jere Wannan Wahalhalun Ba’, ‘Dole A Dawo da tallafin man fetur’.

Gwamnatin tarayya da na jihohi sun yi yunkuri iri-iri da zummar dakatar da zanga-zangar, suna masu cewa zauna-gari-banza da makiya dimokuradiyya za su iya kwace ta, wadda ka iya janyo asara ga kasar.

A baya dai rahotanni sun tabbatar da cewa za a fara zanga-zangar ne ranar Alhamis, 1 ga watan Agustan, 2024.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda