Matasa Sun Kaddamar Da Zanga-Zanga A Jihar Neja

Masu zanga-zanga a Neja

Matasa a Jihar Neja sun kaddamar da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya.

Masu zanga-zangar sun fantsama kan manyan titunan jihar, ciki har da babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna.

Matasan da ke tafe suna rera wakar adawa da tsare-tsaren gwamnati sun daga kwalaye masu dauke da rubutu a jikinsu da ke nuna bacin ransu kan halin tsadar rayuwa a Najeriya.

A jikin kwalayen sun yi rubuce-rubuce da dama, da suka hada da, ‘A soke tsare-tsere masu kuntata wa jama’a; ‘tura ta kai bango’; ’ ‘Mu Ba Bayi Ba Ne A kasarmu’; ‘Ba Za Mu Jere Wannan Wahalhalun Ba’, ‘Dole A Dawo da tallafin man fetur’.

Gwamnatin tarayya da na jihohi sun yi yunkuri iri-iri da zummar dakatar da zanga-zangar, suna masu cewa zauna-gari-banza da makiya dimokuradiyya za su iya kwace ta, wadda ka iya janyo asara ga kasar.

A baya dai rahotanni sun tabbatar da cewa za a fara zanga-zangar ne ranar Alhamis, 1 ga watan Agustan, 2024.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya