Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana

Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun sakandaren kwana a matsayin wani mataki na kariya ga ɗaliban makarantun.

A cikin wata sanarwa da Mamman Mohammed, kakakin gwamnan, ya ce, wannan shawara ta biyo bayan taron tsaro tsakanin Gwamna Mai Mala Buni da shugabannin tsaro a jihar, inda suka yi nazari kan abubuwan da suka faru na tsaro a makarantu a wasu sassan ƙasar nan.

Sanarwar da Babban Sakatare na ma’aikatar Ilimi na Jihar, Dakta Bukar, ya sanya wa hannu, ta umarci a rufe dukkan makarantun sakandare na kwana nan take har sai an samu ci gaba a lamarin.

Gwamna Buni ya yi kira ga al’ummar jihar da su yi wa shugabanni, jami’an tsaro, addu’ar ci-gaba da samun zaman lafiya da ingantaccen tsaro a Jihar da ma ƙasar baki ɗaya.

Daga sai gwamnan ya yi fatan alheri ga ɗaurewar harkokin tsaron Jihar tare da bayar da tabbacin ci gaba da kula da harkokin tsaro da rayukan al’ummar jihar ta kowace fuska kuwa

Post masu alaƙa

Zulum ya bai wa sojoji kyautar motocin yaƙi, ya tallafa wa ’yan gudun hijira

Yan bindiga sun lafta wa manoma sabbin haraji a Sakkwato

Wasu Tsiraru Ne Ke Rura Matsalar Tsaro A Najeriya — Christopher Musa