Mutane 7 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jigawa

Wani mummunan hatsarin mota da ya faru a Jihar Jigawa ya yi sanadin mutuwar mutane bakwai ciki har da direban motar tare da jikkata wasu 11.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Shiisu Lawan Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya aike wa manema labarai a Dutse.

Ya ce hatsarin ya afku ne da misalin ƙarfe 4:30 na yammacin Lahadi, 16 ga Nuwamba 2025, a ƙauyen Jigawan Kurma da ke kan titin Kiyawa zuwa Azaren Jihar Bauchi.

A cewar SP Shiisu, “Mota kirar Hummer ce da ta taso daga Kano zuwa Potiskum ɗauke da fasinjoji 18. Hatsarin ya faru ne bayan fashewar tayoyi biyu, sakamakon gudun wuce sa’a da direban yake yi.”

Ya ƙara da cewa sauran 11 da suka samu munanan raunuka an garzaya da su babban asibitin Birnin Dutse, inda aka sallami huɗu daga cikinsu bayan samun kulawa.

 

Post masu alaƙa

Alarammomi sun amince da tsarin haɗa ilimin boko da na addini a Jigawa

Gwamnati za ta mayar da yara 5,000 makaranta a Jigawa

Ba mu ƙarƙare batun sauya kayan NYSC ba – Ministan Matasa