Najeriya na ƙara sa ido bayan ɓarkewar Ebola a Congo

Ebola virus, illustration.

Hukumar Daƙile Yaɗuwar Cututtuka a Najeriya, NCDC ta ce duk da cewa ba a samu ɓullar cutar Ebola ba a ƙasar, tana ƙarfafa matakai don sa ido sakamakon mutuwar mutum 88 a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo da kuma samun mutum guda da aka bayar da rahoton ya kamu da cutar a Uganda.

Cikin wata sanarwa da Darakta Janar na hukumar, Jide Idris ya fitar a ranar Lahadi, hukumar NCDC tana shirya ayyukan wayar da kai da kuma a faɗin ƙasar.

Matakin na zuwa ne yayin da Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO ta ayyana ɓarkewar Ebola a Congo da Uganda a matsayin babban abin damuwa.

Hukumomin lafiya ta ce ɓarkewar cutar tana ɗauke da babban haɗari saboda tuni aka gano ƙwayar cutar a Uganda sannan kuma an samu mutanen da suka kamu a Kinshasa da ke Congo.

Cutar da ta fara ɓulla a Lardin Ituri na Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo ta shafi kusan mutum 246.

Post masu alaƙa

Kwankwaso Ya Ja Girmansa Ko Na Fara Mayar Da Martani — Abba Kabir Yusuf

DSS ta sake gurfanar da El-Rufai kan zargin satar bayanai ta wayar Ribadu

Sabbin hare-haren sojojin Najeriya ya kashe mayaƙan ISIS fiye da 20