Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5

Nijeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan sabuwar yarjejeniyar fahimtar juna ta shekaru biyar (MoU) don karfafa hadin gwiwar tsaro a tsakanin kasashen biyu.

Yarjejeniyar, wacce aka sanar a ranar Talata a cikin wata sanarwa da Ahmed Dan Wudil, Mataimaki na Musamman kan Yada Labarai ga karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya fitar, ta bayyana cewa, hadin gwiwar ta shafi dabarun horar da sojoji, raba bayanan sirri, samar da tsaro, da ayyukan hadin gwiwa.

An sanya hannu a yarjejeniyar ne a Riyadh ta hannun Ministan Tsaro na Nijeriya, Matawalle, da Dr. Khaleed H. Al-Biyari na Saudiyya, ana sa ran yarjejeniyar za ta zama tsarin ci gaban tsaro mai dorewa a fadin kasashen biyu.

Post masu alaƙa

Yar Najeriya ta kammala jami’ar Burtaniya da daraja ta daya (1st Class) a ilimin kimiyar samar da manhajar kasuwancin zamani.

Gwamnati ta buƙaci jama’a su guji taɓa kumfar da ta ɓulla a hanyar Kaduna-Abuja

A riƙa yi wa masu shirin aure gwajin miyagun ƙwayoyi :- Buba Marwa