NNPC Ta Tabbatar da Cewa Tana da Isasshen Man da Zai Wadatar da ‘Yan Najeriya

Kamfanin mai na NNPC, ya ce jama’a su daina fargaba domin akwai wadataccen mai a kasa

Wannan na zuwa ne bayan da aka fara samun layin mai da aka fara dogayen layuka a gidajen mai a wasu sassa na Najeriya bayan sanarwar cire tallafin mai da sabon shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu ya ce zai yi.

Shugaban kamfanin, Malam Mele Kyari, ya ce, akwai mai don haka babu wata matsala da ya ke gani za a iya fuskanta da ta shafi karancin man.

Ya ƙara da cewa dama duk lokacin da aka samu irin wannan jawabi daga shugabanni, sai mutane su yi ta tururuwa suna zuwa gidajen mai suna siyan mai fiye da wanda suke bukata

saboda suna tsoron kada a kara kudin man a cewar.

Ya kara da cewa bai ga abin tsoro ba domin akwai mai sosai a kasa.

Post masu alaƙa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga

JIBWIS Gwallaga Sun Ziyarci A Sansanin Alhazai Na Jihar Bauchi Domin Bada Agaji

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro