Shugaba Tinubu Ya Ayyana Sunayen Mutane 3 a Matsayin Hadimansa

Zaɓaɓɓen shugaban ƙasar nan, Bola Ahmad Tinubu, ya ayyana sunanayen wasu mutane uku a matsayin masu taimaka masa cikin ƙunshin gwamnatinsa wacce ta fara a yau.

Mutanen da shugaban ƙasar ya naɗa sun haɗa da:

Ambasada Kunle Adeleke a matsayin cif-furotakwal na shugaban ƙasa.

Sai kuma tsohon kwamishinan labarai na jihar legas, Dele Alake, a matsayin mai Magana da yawun shugaban ƙasa.

Na ukun shi ne Olusegun Dada a matsayin mashawarci na musamman ga shugaban ƙasa kan kafafen sada zumunta na zamani.

Ana sa ran cewa shugaban ƙasar zai kammala naɗe-naɗensa ne cikin kwanaki 60 kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada wanda ya haɗa da muƙaman da ke buƙatar sahalewar majalisun ƙasar nan.

Post masu alaƙa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga

JIBWIS Gwallaga Sun Ziyarci A Sansanin Alhazai Na Jihar Bauchi Domin Bada Agaji

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro