Tawagar da Majalisar Ɗinkin Duniya ta tura zuwa Najeriya don gudanar da bincike a game da zargin kisa da yin garkuwa da mutane da kuma tilasta wa wasu mutanen barin muhallansu saboda dalilai na addini, ta ce waɗannan zarge-zarge ba gaskiya ba ne.
Jagorar tawagar Farfesa Nazila Ghanea, ita ce ta sanar da hakan bayan ziyarar gani da ido ta kai a ƙasar, inda ta ce mutane na yin waɗannan zarge-zarge ne saboda gazawar gwamnati wajen ba su kariya da kuma gaza hukunta waɗanda ke aikata laifukan. Ga dai abin da Farfesa Ghanea ke cewa.