Ramadan: Ƙanƙara Ta Zama ‘Yar Sarki a Kano

A yayin da ake kai azumi na shida a yau, al’umma na cigaba da nuna damuwa game da farashin ƙanƙara wanda sukan yi amfani da ita domin sanyaya abin sha a lokacin buɗa baki.

Su ma masu sana’ar sun bayyana wa abokiyar aikinmu irin ƙalubalen da suke fuskanta, musamman a lokacin da ake fama da ƙarancin wutar lantarki da tsadar kayan alkinta ƙanƙara da makamantansu.

Har’ila yau wani masanin lafiya yi mana ƙarin haske kan matsayin amfani da ƙanƙara a lokacin buɗa baki a wannan watan na ramadana.

Ga abokiyar aiki Zubaida Abubakar Ahmad da rahoton da ta haɗa mana.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM