• Home  
  • Rusau: Gwamnatin Kano Ta Rushe Wani Gini Dake Daula Otel
- Labarai

Rusau: Gwamnatin Kano Ta Rushe Wani Gini Dake Daula Otel

Sabon gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya cigaba da abin da ya yi alkawari na karbe filaye gwamnati da aka yi gine-gine a kan su. A daren Lahadin nan, labari ya zo daga gidan rediyon Freedom cewa gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta ruguza gini da aka yi a otel da ake kira da Daula.

Daula Hotel

Sabon gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya cigaba da abin da ya yi alkawari na karbe filaye gwamnati da aka yi gine-gine a kan su. A daren Lahadin nan, labari ya zo daga gidan rediyon Freedom cewa gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta ruguza gini da aka yi a otel da ake kira da Daula.

Sabon Gwamnan ya na ikirarin an yi wadannan gine-gine ne ba a kan ka’ida ba, don haka tun kafin ya dare kan kujera, ya sha alwashin kai su kasa

Tun a ranar Asabar, sabon Gwamnan ya bada umarnin rusa duk ginin da ya sabawa ka’idar jiha.

Kamar yadda  sakataren yada labaran na gwamna Sanusi bature  Dawin-Tofa ya fitar,inda yace, gwamnati ba za ta yarda da gini a makarantu, kasuwanni, asibitoci da duk wuraren al’umma ba domin  yin hakan zai dawo da kimar jihar sannan zai tabbatar da tsari tare da kawata wuri da inganta tsaro.

A gefe guda, wannan ya jawo surutu daga wasu mutane da suke ganin an jawowa jama’a asara.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai