Ruwan Sama Ya Haddasa Ambaliya A Makka 

A garin Makkah, hotunan da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna yadda ruwa ya mamaye hanyoyi, lamarin da ya hana jama’a zirga-zirga.

A wasu wurare, ruwa ya shanye motocin jama’a, wanda hakan ya jefa su cikin mawuyacin hali.

A unguwar Al-Awali, wasu maza sun yi ƙarfin hali domin ceto yaran da suka maƙale sanadin wannan ambaliyar.

Sun haɗa hannu suna taimaka wa juna wajen fitar da yaran daga mawuyacin halin da suka tsinci kansu.

Wannan bai tsaya nan ba, rahotanni sun bayyana cewa wasu a wuraren an gidaje sun rushe, yayin da kayan abinci suka lalace.

A birnin Jeddah, an samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya, wanda ya tilasta wa hukumomi dakatar ds zirga-zirgar jiragen sama a wasu filayen jiragen sama.

Wannan ba shi ne karon farko da Saudiyya ke fuskanci irin wannan yanayi ba.

A shekarar 2009, birnin Jeddah ya fuskanci ambaliyar ruwa mai tsanani, wanda ya janyo mutuwar mutum sama da 100 tare da lalaga gidaje da tituna.

Har ila yau, a shekarar 2020, wasu wurare a ƙasar sun fuskanci irin wannan matsalar sakamakon ruwan sama kamar da bakin ƙwarya.

Post masu alaƙa

Nafi’u ya gargaɗi Atiku ya daina sukar Tinubu da sunan ADC

Yan Sandan a Kano sun kama mutane 244, ciki har da 117 da ake zargi da fadan daba.

Ƴansanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a bikin Takutaha, tare da gargaɗin masu yunkurin tada zaune tsaye.