Sakataren Harkokin Wajen Amurka Ya Kai Ziyarar Aiki Kasar Sin

Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken na ci gaba da ziyararsa ta kwana biyu a Beijing babban birnin China.

Wannan ziyara ita ce ta farko da waji babban jami’in diflomasiyya daga Amurka ya kai China cikin kimanin shekara biyar.

Jami’an Amurka sun ce babban maƙasudin ziyarar shi ne tattauna alaƙar kasarsu da China, wadda ta ke zama mai tsami a kullum.

Ziyarar na zuwa ne watanni biyar bayan ɗaga ziyarar farko da Blinken ya shirya zuwa, bayan kama wani balabalan ɗin leƙen asiri da ake zargin na China ne a sararin samaniyar Amurka.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr