Ministan harkokin wajen Saudiyya ya tattauna da shugaban kasar Iran

Ministan harkokin wajen Saudiyya Faisal Bin Farhan, ya isa Tehran tare da tattaunawa da shugaban Iran da kuma Ministan harkokin waje Ebrahim Raisi da Hossein Amir Abdolliah.

Wannan ce zaiyarar farko da wani babban jami’in Saudiyya ya kai Iran cikin shekara bakwai da ƙasashen biyu suka yanke alaƙa da Juna.

A yau, an yi taron ‘yan jarida na haɗin gwiwa tsakanin Ministan harkokin wajen Saudiyya da kuma Amir Abdolliah.

A tattaunawar, Faisal Bin Farhan ya ce ziyarar tasa na da nufin kammala duka yarjeniyoyin ƙasashen biyu a wani ɓangare na sabunta alaƙarsu.

Post masu alaƙa

Gwamnati ta buƙaci jama’a su guji taɓa kumfar da ta ɓulla a hanyar Kaduna-Abuja

Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kwace kadarorin Godwin Emefiele

Dalibai huɗu za su wakilci Najeriya a gasar Spelling Bee ta Duniya a China