Masarautar Saudiyya ta ba wa ɗaliban Najeriya 50 guraben karatu cikakku a fannonin albarkatun man fetur da ma’adinai.
Jakadan Saudiyya a Najeriya, Yousef Bin Mohammed Al-Balawi, ya bayyana cewa shirin guraben karatun ya haɗa da kuɗin makaranta, tikitin tafiya, masauki da kuma alawus na wata-wata a Jami’ar Man Fetur da Ma’adinai ta Sarki Fahd.
Jakada Al-Balawi ya sanar da ɗaukar nauyin ɗaliban a lokacin ziyarar da ya kai ofishin Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai na, Mohammed Idris, a Abuja ranar Talata.
Ya ƙara da cewa tuni ƙasarsa ta riga isar da tayin guraben karatun ta wata takarda daga Jami’ar Man Fetur da Ma’adinai ta Sarki Fahd.
“Wannan shiri yana nuna kyakkyawar alaƙa mai ƙarfi tsakanin Saudiyya da Najeriya. Haɗin gwiwa ne na gaskiya da kuma zuba jari a makomar matasan Najeriya,” in ji jakadan.
Ya kuma sake jaddada ƙudirin ƙasar Saudiyya na haɗin gwiwar ilimi a matakin ƙasa da ƙasa da Najeriya.
Da yake magana a yayin ganawar, ministan ya nuna matuƙar godiyar Najeriya bisa wannan shiri na guraben karatu, yana mai cewa ya yi daidai da manufofin Gwamnatin Tarayya na bunƙasa muhimman sassan tattalin arziki ta hanyar inganta ƙwarewar ma’aikata.
“Wannan ba kawai shirin bayar da guraben karatu ba ne; wata muhimmiyar zuba jari ce ga makomar Najeriya, musamman a muhimman ɓangarorin kamar man fetur da ma’adinan ƙasa da ke da matuƙar tasiri ga ci gaban tattalin arzikinmu da kuma faɗaɗa hanyoyin samun kuɗin shiga,” in ji shi.
Ya kuma jaddada muhimmancin shirin, yana mai cewa ana sa ran za a riƙa aiwatar da shi a kowace shekara, wanda hakan zai haifar da tasiri mai ɗorewa.
“Kasancewar an tsara shirin ya riƙa gudana a kai a kai, inda ɗalibai 50 daga Najeriya za su riƙa amfana a duk shekara, hakan zai tabbatar da samar da ƙwararru masu kwarewa a muhimman masana’antunmu,” in ji shi.
Minista Idris ya kuma tabbatar wa jakadan ƙudirin Najeriya na ƙara danƙon zumunci tsakanin ƙasashen biyu tare da hanzarta aiwatar da yarjejeniyoyin da ke tsakaninsu.
“Gwamnati na da ƙudirin karfafa wannan haɗin gwiwa tare da tabbatar da aiwatar da dukkan yarjejeniyoyin da ke akwai, ciki har da waɗanda ake shirin ƙullawa a ɓangaren yaɗa labarai da sauran fannoni domin amfanin juna,” in ji shi.
Har ila yau, ministan ya yi amfani da damar wajen nuna goyon bayan Najeriya ga Saudiyya ɗangane da rikice-rikicen da ke faruwa a yankin Gulf, yana mai fatan samun zaman lafiya da kwanciyar hankali.
“A madadin Gwamnatin Tarayya, muna nuna goyon bayanmu ga Masarautar Saudiyya a wannan lokaci na taƙaddama a yankin Gulf. Muna fatan a samu ɗorewar zaman lafiya da warware matsaloli ta hanyar diflomasiyya,” in ji shi.
Tun da farko, Jakada Al-Balawi ya isar da godiyar shugabannin Saudiyya ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa goyon bayan da ya nuna, yana mai cewa hakan na ƙara nuna ƙarfin alakar da ke tsakanin ƙasashen biyu